XtGem Forum catalog
Darus-sahaba
1jojlxKOMkX9WyteRe4hGfd...5Tlzwos6Wa8pU99NjJEjmoO7lE72qs...P8zLBUI5VEdw01bf9Bj3WN2UJZQ0kMkumqAOI9CU319yy4DVw
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka

wanna shafi yana zuwa muku kai tsaye daga masallacin jumu'a
Jami'u Abu hurairah
Dake kurna y'an kifi titin y'an smogal a karamar hukumar dala dake kano Nigeria
kar kashin jagorancin
Sheik Muhammad Sani Uthman Kurna

Home
Karatut-tukan Sheik Muhammad Thani Uthman Kurna
Mata A Musulunci
Bayanin Zakka
Bayanin Azumi
Bayanin Hajji da Umara
Kasuwanci mai ribar gaske
Muhimmin Sako Zuwa ga Ma'aurata
Tsarin Mu'amala A cikin Musulunci
Hakkokin Manzon Allah s a w Akan Alumarsa
Shin hadin kai zai yiwu tsakanin Ahalussunnah da shi a
Wadanna mata aka Haram tawa musulmi da kuma wanda aka Halarta
Hukunce - Hukunce da suka shafi mata
Jinin Al ada ga mata
Jagoran mai wa azi
Adduo in manzon Allah s a w
Falalar Karatun Al-kur'ani
Falalar Sahabbai {R.A}
Falalar Sahabbai {R.A} Daga bakin Imamai
Tarihi
Falalar Ahlulbait daga bakin Ahlussunnah
Tambayoyi masu muhimmanci A cikin Addinin Musulunci
Ayyukan Zuci
Tattaunawa Ta Nitsuwa
Addinin Shi'a
Hukunce-Hukuncen Da Suka Shafi Mata
Karatut-tukan Malamai da Lakcocin su



2014-11-09

-----------------------------------
FALALAR KARATUN AL QUR`ANI

KASHI NA UKU 3

SAKAMAKON.WANDA YARONSA YA KOYI KARATUN AL QUR`ANI

MANZON ALLAH SAW YA CE"wanda ya karanci al qur`ani kuma ua san shi ya kuma yi aiki.da shi za a sanyawa iyayensa,biyu hular girma ta haske ranar tashin kiyama,hasken hular kamar hasken rana ne,kuma za a tufatar da iyayensa guda biyu tifafin kwalliya wnda duniya bata kai su daraja ba.dai iyayen guda biyu su ce "dan me aka tufatar da mu wannan kayan?" Sai ace musu "saboda rukun da danku yAyi al qurani,(Hakim).

CETON AL QUR'ANI GA MA'ABOCINSA(MAHADDACINSA)A LAHIRA

MANZON ALLAH S.A.W YA CE"KU KARANTA AL QUR'ANI SABODA ZAI ZO RANAR TASHIN ALKIYAMA YANA MAI CETO GA MA'ABOTANSA" (muslaim).

MANZAON ALLAH S.A.W YA KARA CEWA"AZUMI DA ALQUR'ANI ZASU CETO GA BAWA RANAR TASHIN ALKIYAMA"(Ahmad da Hakim).

LADAN HADUWA KAN TILAWAR ALQUR'ANI DA YIN DARASI A CIKINSA

MANZON ALLAH S.A.W YACE "MUTANE BASU TABA HADUWA BA, A CILIN WANI GIDA DAGA CIKIN GIDAJEN ALLAH(MASALLACI)SUNA KARANTA LATTAFIN ALLAH KUMA SUNA KOYAR DA SHI A TSAKANINSU,FACE SAI NUTSUW TA SAUKA A GARE SU,KUMA RAHAMA TA LULLUBE SU,KUMA MALAIKU SU KEWAYESU,SANNAN KUMA ALLAH YA AMBA CE SU GA WADANDA SUKE WAJENSA WATO (MALAIKU). (Abu dawud)

WASU DAGA HUKUNCE HUKUNCEN KARATU

LADDUBAN KARATUN AL QUR'ANI

IBN KHASIR ya ambaci wani sashi daga cikin ladduban kamar haka yace"kada mutum ya shafi alqur,ani kuma kada ya karantashi face yana tsarki,kuma sannan yayi asuwaki kafin fara karatunshi,kuma ya sanya mafi kyawu daga cikin tufafinsa,kuma ya fuskanci alqibla,ya tsayar da karatunsa yayin himma,kada ya yanke karatunsa domin ko yayin wata magana sai inda bukatar hakan ya halarto da hakalunsa yayin karatun ya tsaya akan kowacce aya,da aka yi magana akan rahama domin ya roki ALLAH wannnan ni,ima,da kuma tsaya akan ayar azaba domin ya nemi tsari akai,kar ya ajiye alqur,ani a warwatse,kar kuma ya dora wani abu akansa,kada kuma wasu sashi na makaranta su daga murya akan karatun wasu sashin,saboda kada a sami rudani kuma kada a karanta shi a kasuwa da wuraren da ake ihu da wasanni.

YADDA AKE KARANTA AL QUR,ANI

An tambayi Anas dan malik r.a kan yadda karatun ANNABI S.A.W yake,sai ya ce

"Ya kasance yana jan maddah idan ya karanta BISSIMILLIHIRRAHMANIRRAHIM yakan yi maddah akan sunan ALLAH kuma ya kan yi maddah akan rahman kuma ya kan yi maddah akan rahim(bukhari).

RIBANYA SAKAMAKON KARATU

Dukkan wanda ya karanta don ALLAH to za,a bashi lada kuma lallai ana rubanya wannan ladan kuma ana girmamashi a lokacin da zuciyarsa take halarce,kuma yana bibiya da kokarin fahimtar abin yake karantawa,sai ya zama a kowanne harafi ana bashi lada goma 10 har e zuwa ninki dari bakwi 700.

GWARGWADON ABUN DA YA KAMATA A KARANTA A KOWNNE YINI DA DARE NA AL QUR,ANI.

SAHABBAN(R.A) MA,AIKI S.A.W sun kasance su na sanyawa kawunansu wani kaso daga cikin alqur,ani a kowacce rana,sukan dauwama akan kokarin karanta shi,duk a cikin kena bakwai 7,a,a ha hani yazo akan rashin karanta shi a cikin kwana uku 3,ka yi kwadayi ya dan,uwa wjen tafuyar da lokacinka cikin karatun alqur,ani kasanyawa kanka wani abu daga cikin alqur,ani a kowanne yini,ba zaja bar shi ba ya wuce duk yadda abubuwa suka cabe maka,domin masu iya magana sunce"kadan din da ake yi kullum yafi alheri,fiye da mai yawan da ake yi a gutsutstsure,idan ka manta ko kayi barci baka karanta shi ba,to gobe sai ka rama shi,saboda

MANZON ALLAH S.A.W YACE"WANDA YAYI BARCI AKAN KASON DA YAKE KARANTAWA NA DARE,BAI YI BA KO WANI ABU DAGA CIKINSA,SAI YA KARANTA SHI A TSAKANIN SALLAR ASUBAH KO KUMA SALLAR AZUHUR,TO ZA,A RUBUTA MASA LADA KAMAR YA KARANTA SHI A CIKIN DARE".(muslim)

YA DAN'UWA

Kar ka zama daga cikin wadanda suka kauracewa al qur,ani ko suka manta da shi daga cikin kowanne irin nau,i na kauracewa,kamar nisantar karantashi ko kuma kokarin fahaimtarsa ko kuma kokarin aiki da shi ko kum kokarin neman waraka da shi.

Daga naku ABDULMAJID IBN NUHU
FALALAR KARATUN ALKUR,ANI

( kashi na biyu) (2)

FALALAR KOYON KARATUN ALKU,ANI DA HADDACE SHI DA. KUMA GWANANCEWA WAJEN IYA KARANTA SHI

manzon Allah. (S a.w) ya ce . Misalin mutimin da yake. Karatun. Alkur,ani. Alhali yana mai kiyaye shi (hardace shi) to yana tare da mala, iku masu girma, tsarkaka kuma misalin wanda ya ke karanta shi alhalin yana mai kai komo da shi sa,annan yana mai tsananin wahala a kansa, to yana da sakamako kashi biyu(sakamakon wahalar da kuma karatun ) ( Bukhari da muslim) (Abin da ake nufi da safaratu a cikin. Hadisin su ne mala ,iku.)

Manzon Allah.( S.a.w) yakara cewa.
Ana.cewa ga maabocin Alkur,ani ( wato. ga mahaddacinsai a alkiyama ) karantaa kuma kayi sama. Ka kuma karanta. Kamar yadda ka kasance ka ke karantawa a duniya lallai matsayinka zai tsaya ne a karshen ayar da ka karanta ta. (Turmizi)

ALKHADDABI-ALLAH YA MASA. RAHAMA YACE

Ya zo a cikin maganganun magabata lallai cewa gwargwadon yawan a yoyin Alkur,ani shi ne gwargwadon matsayi agidan Aljanna. Sai a ce wa mai karatun Alkur,ani ka yi sama gwargwadon abin da ka kasance kana karantanwa (haddacewa) na ayoyin Alkur,ani duk wanda yakaranta. Alkur,. dukkansa to shi zai samu mafi. girman daraja a gidan aljanna a. Ranar lahira wanda kuma ya karanta juzu,i daya daga cikinsa darajarsa za ta kasance gwargwadon abin daya karanta. Sai ya zama gwargwadon ladanka gwargwadon inda karatun ya tsaya.
`.............``.............. .................................. ................................................................................... muhadu a kashi na gaba
FALALAR KARATUN ALKUR,ANI

Dukkan yabo ya tabbata ga ALLAH kuma tsira da amincin Allah su tabbata ga shugbanmu manzon Allah da kuma Alayensa da sahabbansa amma bayan haka lallai Alkur'ani zancan Allah ne kuma falalarsa akan sauran maganganu kamar daukakar Allah ne akan halittunsa karana shi kuwa shi ne abin dayafi falala kan dukkan abin da harshe ke motsi da shi.

KOYON KARATUN ALQUR,ANI DA KOYAR DA SHI DA KARATAR DA SHI YANA DA FALALA MAI YA WA: daga ciki

SAKAMAKON KOYAR DA SHI: Manzon Allah(s.a.w) ya ce mafi alhernku shi ne wanda ya koyi Alqur'ani kuma ya koyar da shi.(bukhari)

SAKAMAKON KARANTA SHI : Manzon Allah (s.a.w) ya ce duk wanda ya karanta harafi daya daga cikin littafin Allah yana da ladan wannan harafi kuma shi ladan za a ninka shi sau goma (turmizi)

mai ga ba tarwa ABDULMAJID IBN NUHU

Muhadu a kashi nagaba



Kuna iya tuntu6ar mu ta wadannan hanyoyin
Abdul-majid Ibn Nuh ta face book

KO TA SHAFIN MU NA FALALAR SAHABBAI DAGA BAKIN IMAMAI TA FACE BOOK.

Ko ta watsAp A 07063276717
Bugo mana waya ta nan
Bugo mana waya ta nan
Bugo mana waya ta nan
Ko ta Email A

Home


Copyright © 2014 - 2015By:- Abul-majid Ibn Nuoh Powered by- Basheer journalist sharfadi